Ma’aurata: Shin Kasan Abunda Akeyiwa Amarya A Daren Farko

 


Ma’aurata: Shin Kasan Abunda Akeyiwa Amarya A Daren Farko


DAREN FARKO


 


.SOYAYYA CE KO MUGUNTA:


.


Bayan sallar isha’i da wuri ango Ahmad


ya koma gida, daga nan suka shiga daki,


daga nan kuma ango ya kulle daki yayin da


Amarya mai suna Hafsat kuwa tana zaune


akan gado kanta lullube da kyalle.


.


Daga nan kuma Ango ya karaso gareta


ya yaye mayafi, aikuwa amarya ta dago fuska


da murmushin ta, bisa mamaki sai taga


ango ya turbune fuska, hankalinta bai tashi ba


sai data ga ya zaro bel dinsa yana nannadewa a hannu, take kanta ya kulle dan bata san miye manufarsa ba.


.


Kan kace me ango ya hau amarya da duka


yana zaneta da bel tun tana ihu harta rasa bakin kuka, jim kadan jikinta duk ya tattashi


amarya sai sheshshekar kuka.


.


Bayan nan kuma ango ya daura ruwan zafi


yayi mata treatment,sai abin ya bata mamaki


ganin ya daketa da hannunsa kuma yana jinyarta.


.


Bayan ta warke ne kuma ta tambayesa meyasa yaimata dan banzan duka haka a darensu na farko?


.


Ahmada yace: “badon komai na zaneki ba illa wahalar dani da kikayi lokacin da na nemi soyayyarki,


na kasa hakura hakan yasa na rama da duka


Kwanciyar Aure.


 


A kasar Hausa aure da dama sun mutu badan Abinciba ko rashin kulawa, A’a maganar Gaskiya muna da karancin wayewa wajen kwanciyar jima’i majority munfi Ɗaukar kwanciya daya da mahimmanci itace wacce mijinki ya hau kanki akwai kwanciya kala-kala wacce akwai citta Acikinta, kuma ita kwanciya tana kara damke aure gam duk da samun lafiyayyen namiji Sa’ane na wata yafi na wata.


 


Kiyi iyayinki ki koyi kalolin kwanciyar Aure domin chanja tunanin mijinki da sace tunaninsa ako da yaushe zuwa kanki, wlh indai kin iya kalolin kwanciyar jima’i koda ƙaddara tasa kun rabu da mijinki to tunaninki zai ta damumsa a lokacin da yake kan wata matar tasa wata rana har kuka sai yayi akanta ita tunaninta dadi gareta shi kuma damuwar kewarki adaidai wannan lokaci.


 


Taku:- Ummu Saratu Yusuf.


ummee.


Talla babban illace ga rayuwan yaa mace ko da kuwa karaman yarinya ce.


Kaman yanda natakaita managar a shafina nace talla ya zama bara zana ga ƴaran mata yanzu, musanman masu sayar da abinci, gyaɗan, pure water, masa, kwankwa mati, ƙwai, kuli kuli, dama rauran su.


Wasu iyayen suna sakawa ƴaran mata talla ne saboda su nima abin da za su ci kuma su kara rufa ma Kan su asiri saboda babu yanda za suyi, amma ana samu wasu iyayen suna sakawa ƴaran su talla ne saboda son abin duniya alhalin Allah ya rufa masu asiri babu shakka wannan babban kuskuri ne ga iyaye mata


Watarana kusan sau uku ina ganin ana zubar da “masa” a bayan gidan mu abin ya sha bani mamaki ina “tambayan” kai na shin wa yake wannan aikin? ya zubar da “masa” masu kyau alhalin bai lalace ba, sai wani lokaci nafito daga gida misalin karfe goma na safe sai nayi ido biyu da mai wannan aikin ashe wata ƴar talla ce idan aka bata talla sai ta zubar da shi, kuma ba karaman yarinya ce ba budurwa ce take wannan aikin. sai na “tambaye ta” ko me dalili idan aka baki talla kina zubar da shi? sai tace ai wani Alhaji ne yana mani juye kullu idan nafito wurin sa nake zuwa sai ya min juye kuma yakara bar mani “masan” shi yasa nake zubar da shi domin kuwa idan bai kare ba mamana sai tayi mani kukan tsiya, sai abin ya bani mamaki da tace wani Alhaji ne yana yi mata juye kullu


Da yawa iyaye mata suna kuskure ki baiwa yarinya talla kice kar ki yarda ki dawo da wani abu agidan nan sai ya kare wannan kuskuri ne babban saboda wannan kalma yana iya sa yarinya ta fa ɗi daga sherrin zina saboda tana tsoron kar ta dawo da wani abu, tana iya bayar da kan ta domin ta samu kuɗin da zata baiwa wace ta bata talla gudun kar ta sha dukan tsiya.


Comments

Popular posts from this blog

Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Yanzu Yanzu Anga Jijirin Wata Ramadan a Kasar Saudiyya Gobe Insha Allahu Zamu Tashi Da Azumi Wata Ramadan Kareem Ya Allah Duk Alkhairin Dake Cikin wannan Wata Allah Ubangiji Kasadamu Dashi Sharrin Kuma Dake Cikinsa Allah Ubangiji Ya Karemu Ya Allah Kasa Muda Daga Cikin Bayinka Wadanda Kake Yan Tawa A Cikin Wannan Wata Mai Albarka Alfarmar Annabi Muhammad S 💔 A 💔 W 💔 Ameeeen Thumma Ameeeen 🤲🤲🤲