Rahotanni daga ƙasar Saudi Arabia na cewa jami'an tsaron ƙasar sun cafke mutumin da ya zagi Nana Aisha matar MANZON ALLAH SAW a harabar masallacin Madina a lokacin da suke muhawara da wani ɗan ƙasar Pakistan

 

Rahotanni daga ƙasar Saudi Arabia na cewa jami'an tsaron ƙasar sun cafke mutumin da ya zagi Nana Aisha matar MANZON ALLAH SAW a harabar masallacin Madina a lokacin da suke muhawara da wani ɗan ƙasar Pakistan


Jaridar Labaran Hausa ta ruwaito cewa.

Rundunar ‘yan sanda a birnin Riyadh ta tabbatar da kama wani mutumi wanda ya zagi Sayyada Aisha R.A, matar Annabi Muhammad (SAW).

Manjo Khaled Al-kraidis, wanda yanke shine kakakin rundunar ‘yan sandan Riyadh, ya bayyana cewa a wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sadarwa, an gano cewa bidiyon cin mutuncin ne ga Annabi Muhammad (SAW), haka kuma zagi ne ga uwar muminai, Aisha (R.A).

Bayan kama mutumin an gabatar dashi a gaban kotu domin yanke masa hukumcin daya dace da shi.

An wallafa bidiyon ne a shafukan sadarwa a ranar 10 ga watan Muharram, a lokacin da ‘yan kungiyar Shia suke nuna bakin cikinsu kan kisan da aka yiwa Sayyadina Hussain a lokacin yakin Karbala.

A Musulunci, duka matan Annabi Muhammad guda 11 ana daukar su a matsayin iyaye a Musulunci, a ka’ida ma Musulmai suna so da kuma girmama su fiye da iyayen da suka haife su.

kallai wannan videon 

👇👇👇👇



Comments

Popular posts from this blog

Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Yanzu Yanzu Anga Jijirin Wata Ramadan a Kasar Saudiyya Gobe Insha Allahu Zamu Tashi Da Azumi Wata Ramadan Kareem Ya Allah Duk Alkhairin Dake Cikin wannan Wata Allah Ubangiji Kasadamu Dashi Sharrin Kuma Dake Cikinsa Allah Ubangiji Ya Karemu Ya Allah Kasa Muda Daga Cikin Bayinka Wadanda Kake Yan Tawa A Cikin Wannan Wata Mai Albarka Alfarmar Annabi Muhammad S 💔 A 💔 W 💔 Ameeeen Thumma Ameeeen 🤲🤲🤲