An Kama Masu Gadin Makabarta Suna Tono Kaburburan Mutane


 

An Kama Masu Gadin Makabarta Suna Tono Kaburburan Mutane

Wasu masu gadin makabarta biyu sun shiga hannu inda aka kama su da kawunan dan Adam da suka hoto da cikin kabari.



Dubunsu ta cika ne bayan mutanen unguwa suka kama daya daga cikin mutanen [da ake kira Alhaji] da kawunan mutane a cikin jika.

Wani mazaunin unguwar ya ce, β€œJiya (Lahadi) da safe wani ya shiga jeji yin ba haya shiya sai ya ga Alhaji da wata katuwar guduma yana fasa wani kabari.

β€œDaga baya da Alhaji ya fito da wata jika sai mutumin ya daga kara, sai muka yi maza muka je; muka bincika sai muka ga kan mutun a cikin jikar.

Majiyar ta ce daga baya jami’an tsaron Amotekun sun je sun binne kawunan a unguwar Surulere da ke garin Ondo, Jihar Ondo.

Kwamandan Rundunar [yankin Kudu maso Yamma] Amotekun, Cif Adetunji Adeleye ya tabbatar da tsare mutanen da ake zargin da ya ce jami’ansa sun iske mutanen unguwa na dab da aika su lahira.

Sai dai ya ce ba a samu kawunan mutane ba a tare da mutanen da aka kama kamar yadda ake zargi.

β€œJami’anmu sun kubutar da mutanen da ake zargin ana dab da hallaka su, kuma mun mika su zuwa ga ’yan sanda,” inji shi.


Danna vedion

πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡



Comments

Popular posts from this blog

innalillahi Ku Kalli Halin Da Jaruma Hadiza Gabon Ta Shiga Akan Wannan Iftila'in Daya Faru Danna Hoton Kaga Cikakken Bayani

Innalillahi wa inna ilaihir Raji’un Masu garkuwa da mutane sun kashe Nabeeha saboda yan’uwan ta sun gaza hada kudin fansa Allah yajikan ta da rahama Dalibar ABU ZARIA 400Level Su Shida Aka Sace Tare Da Yan Uwanta Ita Sun Kashe Ta Yanzu Sauran Kannenta Guda Biyar Suna Hannu Su Don Allah Jama'a Ga Account Number A Taimaka A Kubutar Da Wadannan Kananan Yaran

DUNIYA BUDURWAR WAWA; Kalli jerin jaruman kannywood su 16 da kannywood ta juya musu baya suka zama abin tausayi.