Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya shawarci Hukumar Kwastam da sakar wa ’yan kasuwa mara su yi fitsari. Ya kamata a sakar wa ’yan kasuwa mara matuΖar harkokinsu na kasuwanci ba su saba ka’ida ba. Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya shawarci Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa da ta Ζyale ’yan kasuwa su riΖa gudanar da harkokin kasuwancin su ba tare da tsare musu kayansu ba matuΖar ba su karya doka ba. Wannan dai na Ζunshe ne cikin wata sanarwar ranar Litinin mai Ιauke da sa hannun Sakataren yada labarai na Masarautar Kano, Abubakar Balarabe Kofar Na’isa. Sarkin ya yi wannan kira ne a yayin da ya karΙi bakuncin Mataimakiyar Babban Kwamandan Kwastam na Kasa mai kula da shiyyar Kano, Katsina, Kaduna da Jigawa, Queen Ogbudu da tawagarta a fadarsa. Alhaji Aminu Ado Bayero wanda ya bayyana cewa a baya jami’an Hukumar Kwastam suna shiga kasuwanni su karΙe wa ’yan kasuwa kaya ba bisa ka’ida ba, amma yanzu ya ji daΙi da hakan ya zama tarihi. Haka kuma, Sarkin y