Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya shawarci Hukumar Kwastam da sakar wa ’yan kasuwa mara su yi fitsari. Ya kamata a sakar wa ’yan kasuwa mara matuƙar harkokinsu na kasuwanci ba su saba ka’ida ba. Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya shawarci Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa da ta ƙyale ’yan kasuwa su riƙa gudanar da harkokin kasuwancin su ba tare da tsare musu kayansu ba matuƙar ba su karya doka ba. Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwar ranar Litinin mai ɗauke da sa hannun Sakataren yada labarai na Masarautar Kano, Abubakar Balarabe Kofar Na’isa. Sarkin ya yi wannan kira ne a yayin da ya karɓi bakuncin Mataimakiyar Babban Kwamandan Kwastam na Kasa mai kula da shiyyar Kano, Katsina, Kaduna da Jigawa, Queen Ogbudu da tawagarta a fadarsa. Alhaji Aminu Ado Bayero wanda ya bayyana cewa a baya jami’an Hukumar Kwastam suna shiga kasuwanni su karɓe wa ’yan kasuwa kaya ba bisa ka’ida ba, amma yanzu ya ji daɗi da hakan ya zama tarihi. Haka kuma, Sarkin y